DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban jam’iyyar APC a Nijeriya Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya karbi ‘yan jam’iyyun PDP, NNPP, PRP, da suka sauya sheka zuwa APC a jihar Katsina

-

 

Dikko Umar Radda/Abdullahi Umar Ganduje

Google search engine

Wadanda suka sauya shekar yawancin sun fito ne daga jam’iyyar PDP, NNPP, Accord Party, da Jam’iyyar PRP.

Guda daga cikin wadanda suka sauya shekar shi ne dan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a jam’iyyar PDP a zaben 2015 Rabiu Bakori.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje tare da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ne suka karbi wadanda suka sauya sheka a yayin kaddamar da yakin neman zaben kananan hukumomin jam’iyyar APC da aka gudanar a karamar hukumar Ingawa a ranar Lahadi.

Ganduje, ya bayyana ranar a matsayin rana mai girma da tarihi a jihar Katsina, ya kuma ba da tabbacin cewa za a yi wa wadanda suka sauya sheka adalci.

 Ya ce jam’iyyar APC ita ce kadai jam’iyyar da ta cancanci shiga da ke yin abin da ya dace ta hanyar isar da ribar dimokuradiyya ga ‘yan kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara