DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na da isassun kuɗin da Shugaba Tinubu zai yi tafiye-tafiye kasashen duniya – Ministan harkokin waje

-

Ministan Harkokin Wajen Nijeriya Yusuf Tuggar, ya ce Nijeriya na da isassun kuɗin da za ta iya daukar nauyin tafiye-tafiyen Shugaba Bola Tinubu zuwa kasashen ketare.

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin shirin siyasa da gidan talabijin na Channels ke gabatarwa.

Google search engine

Wasu ‘yan Nijeriya dai na yin guna-guni kan yadda shugaban kasar ke yin balaguro daga kasa zuwa kasa, ba tare da kasar ta samu wani ci gaba ba.

Sai dai Ministan ya yi watsi da wannan, inda yace ziyarar shugaban ta jawo wa Nijeriya masu zuba hannun jari da suka saka dala biliyan 2 bayan ziyarar da ya kai a ƙasar Brazil.

Tun bayan hawa karagar mulki a shekarar 2023, rahotanni sun ce Shugaba Tinubu ya ziyarci kasashe kusan 19 a tafiye-tafiye 32 kasashen ketare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara