DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji na dab da yi wa Bello Turji ‘Ƙofar Raggo’ – Rundunar sojin Nijeriya

-

Rundunar sojin Najeriya ta ce nan ba dadewa ba ƙasurgumin dan ta’adda Bello Turji zai zo hannu.
Jami’in yada labaran rundunar ta operation Fansar Yamma Laftanal Kanal Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da makaman da rundunar ta ƙwace daga ‘yan bindiga a karamar hukumar Kaura -Namoda dake jihar Zamfara.
Abubakar ya ce Turji na cigaba da wasan buya tsakaninsa da rundunar, sai dai ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya rundunar za ta kamo shi.
Jami’in ya yaba tare da godewa al’umma bisa hadin kai da bayanan sirri da suke bai wa rundunar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban hafsan sojin kasa ya umurci sojoji da su tsaurara wajen ganin sun ceto dalibai mata da aka sace a jihar Kebbi

Babban hafsan rundunar sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun Operation Fansan Yamma da su matsa kaimi wajen ceto daliban GGCSS Maga da...

’Yan bindiga sun sace fasinjoji shida a hanyar Ogobia–Adoka a Benue

’Yan bindiga sun tare wata motar haya suka tafi da fasinjoji shida sannan suka kashe direba a hanyar Ogobia–Adoka da ke ƙaramar hukumar Otukpo a...

Mafi Shahara