DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji na dab da yi wa Bello Turji ‘Ƙofar Raggo’ – Rundunar sojin Nijeriya

-

Rundunar sojin Najeriya ta ce nan ba dadewa ba ƙasurgumin dan ta’adda Bello Turji zai zo hannu.
Jami’in yada labaran rundunar ta operation Fansar Yamma Laftanal Kanal Abdullahi ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da makaman da rundunar ta ƙwace daga ‘yan bindiga a karamar hukumar Kaura -Namoda dake jihar Zamfara.
Abubakar ya ce Turji na cigaba da wasan buya tsakaninsa da rundunar, sai dai ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya rundunar za ta kamo shi.
Jami’in ya yaba tare da godewa al’umma bisa hadin kai da bayanan sirri da suke bai wa rundunar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara