DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta bai wa iyalan wanda ya zana tutar Nijeriya tallafin milyan 30

-

 

Shugaba Tinubu

Gwamnatin tarayya ta bayar da gudummawar N30m ga iyalan wanda ya yi zanen tutar Nijeriya, Taiwo Akinkunmi, a ranar Alhamis.

Babban daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta kasa Lanre Issa Onilu tare da rakiyar daraktan hukumar na jihar Oyo Olukemi Afolayan ne suka gabatar da cakin kudin a madadin gwamnatin tarayya a fadar gwamnati da ke Elebu, Ibadan, jihar Oyo.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Marigayi Akinkunmi ya rasu ne a ranar 29 ga watan Agustan 2023, yana da shekaru 87 a duniya.

A ranar 4 ga Satumba, 2023, Shugaba Bola Tinubu ya aike da wata tawaga karkashin jagorancin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a Mohammed Idris, domin yi wa iyalan ta’aziyya, inda gwamnatin ta yi alkawarin tallafa wa iyalan marigayin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna kokarin bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 – Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce gwamnatin kasar na kan hanyar bunkasa tattalin arzikin Nijeriya zuwa dala tiriliyan 1 cikin shekaru goma masu zuwa. Kashim...

Yan sanda sun dakile yunkurin garkuwa da direba da fasinjoji a Katsina

Jami’an rundunar ‘yan sandan Nijeriya sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Funtua zuwa Gusau a Katsina. Jami’an sun yi artabu da ‘yan...

Mafi Shahara