DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsare-tsaren gwamnatin tarayya na kara jefa al’umma cikin wahala – Gwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri

-

Gwamnan jihar Adawama Ahmadu Fintiri

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya soki manufofin tattalin arziki da shugaba Tinubu yazo da su,inda ya ce suna takurawa ‘yan Nijeriya, suna shan wahala

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin taron kwamitin sulhu na jam’iyyar PDP na kasa da gwamnonin Arewa maso Gabas suka gudanar da sauran masu ruwa da tsaki a jihar Bauchi

Google search engine

Wadanda suka halarci taron sun hada da gwamnonin Bauchi da Taraba, da kuma mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa Umar Damagun.

Fintiri ya nuna rashin jin dadinsa da yadda halin tattalin arzikin kasar ke tafiya tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta sake duba tsare-tsaren tattalin arzikinta da ke jefa ‘yan Nijeriya cikin matsananciyar wahala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban layin wutar lantarkin Nijeriya National Grid ya fadi

Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya fadi Litinin din nan, lamarin da ya jefa ’yan Nijeriya da dama cikin duhu bayan da manyan tashoshin...

‘Yan bindiga sun kai hari a wani kauye na jihar Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari a kauyen Gebbe da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi, inda rahotanni ke nuna an rasa rayuka yayin da...

Mafi Shahara