DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ba zai iya cin zaben 2027 da tsauraran manufofin sa ba – Shugaban jam’iyyar SDP Gabam

-

 

SDP Chiarman Gabam

Google search engine

Shugaban jam’iyyar SDP a Nijeriya, Shehu Gabam, ya ce tsauraran manufofin tattalin arzikin shugaban Bola Tinubu na iya zama babbar matsala a gare shi idan ya yi yunkurin sake tsayawa zabe a 2027.

Gabam da yake lissafo wasu daga cikin manufofin gwamnatin Tinubu a gidan talabijin na Channels, ya ce cire tallafin man fetur,karin kudin wutan lantarki, da karin kudin sadarwa na daga cikin abubuwanda ka iya ba shi matsala.

Ya kara da cewa Tinubu na bukatar ya sake duba wasu daga cikin manufofinsa, da bukatar ya sauya majalisar ministocinsa idan yana son ya ci zabe domin ba zai iya cin baze da irin wadannan manufofin ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tankiya tsakanin Nijer da Benin ta sa kasashen rufe ofisoshin jakadancin juna

Kasashen Benin da Niger sun kori jami’an diflomasiyyar juna a wani mataki na ramuwar gayya, bayan shafe kusan shekara biyu ana takun-saka a tsakaninsu, a...

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutane fiye da 30 a jihar Neja

Aƙalla mutane 30, ciki har da mata, sun rasu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari Kasuwan Daji da ke ƙauyen Demo, Borgu LGA a...

Mafi Shahara