DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ba zai iya cin zaben 2027 da tsauraran manufofin sa ba – Shugaban jam’iyyar SDP Gabam

-

 

SDP Chiarman Gabam

Google search engine

Shugaban jam’iyyar SDP a Nijeriya, Shehu Gabam, ya ce tsauraran manufofin tattalin arzikin shugaban Bola Tinubu na iya zama babbar matsala a gare shi idan ya yi yunkurin sake tsayawa zabe a 2027.

Gabam da yake lissafo wasu daga cikin manufofin gwamnatin Tinubu a gidan talabijin na Channels, ya ce cire tallafin man fetur,karin kudin wutan lantarki, da karin kudin sadarwa na daga cikin abubuwanda ka iya ba shi matsala.

Ya kara da cewa Tinubu na bukatar ya sake duba wasu daga cikin manufofinsa, da bukatar ya sauya majalisar ministocinsa idan yana son ya ci zabe domin ba zai iya cin baze da irin wadannan manufofin ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun halaka jigo a jam’iyyar APCn jihar Zamfara

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun halaka wani jigo a jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Alhaji Umar Moriki da safiyar ranar Asabar. Gidan talabijin...

Jam’iyyar PDP ta kori su Wike daga cikinta

Jam'iyyar PDP mai hamayya a Nijeriya ta bayyana korar ministan birnin Abuja Nyesom Wike da wasu 'ya'yanta daga cikinta. Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar na yankin kudancin...

Mafi Shahara