DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in Binance cewa ‘yan majalisa 3 sun nemi cin hancin $150m

-

Gwamnatin Nijeriya ta musanta zargin babban jami’in kamfanin Binance Tigran Gambaryan wanda ya shafe watanni takwas yana tsare a hannun hukumomin Nijeriya bisa zargin rashawa.
Gambaryan wanda dan kasar Amurka ne, an sake shi bayan da gwamnatin kasar ta shiga tsakani, sai dai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X ya zargi gwamnatin Nijeriya da tsare shi ba bisa ka’ida ba.
Ya kuma yi zargin cewa wasu ‘yan majalisa uku sun nemi ya basu cin hanci na dala miliyan 150.
A martanin gwamnatin, ta hannun ministan yada labarai Mohammed Idris, ta ayyana kalaman a matsayin yunkurin yada labaran karya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

DCL Hausa na Neman Ma’aikata a Kano (Full-Time)

  DCL Hausa na gayyatar ƙwararru masu jajircewa domin cike guraben aiki na cikakken lokaci (full-time) a ofishinta da ke Kano. Ana neman mutane masu kwarewa,...

Mataimakin kwamishina ya ce ga garinku nan bayan ya fadi a jihar Ebonyi

Wani Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Ogbon-Inu Taiwo Popoola, ya mutu a Jihar Ebonyi yayin da yake halartar taron shugabanci a hedkwatar rundunar ‘yan sanda da...

Mafi Shahara