DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kayan aikin dake filin jirgin saman Legas tsofaffi ne, akwai buƙatar yin gyara cikin gaggawa – Ganduje

-

 

Ganduje

Google search engine

Shugaban hukumar gudanarwa ta hukumar kula da filayen jiragen sama ta Nijeriya FAAN, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada bukatar gyara filin jirgin saman Legas na Murtala Muhammed cikin gaggawa saboda kayan aikin da ke filin jirgin saman sun tsufa.

Yayin ziyara ta farko da ya kai tare da rakiyar babbar daraktar hukumar ta FAAN, Olubunmi Kuku, Ganduje ya tabbatar da cewa yawancin kayan aikin filin jirgin sun lalace.

Ganduje ya kuma bayar da tabbacin cewa hukumar za ta hada kai da hukumomi domin inganta filayen jirgin sama ta yadda za su yi gogayya da na duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ana zargin ‘yan bindiga da sace budurwa sa’o’i kadan kafin daurin aurenta a jihar Sokoto

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kutsa kauyen Chacho a karamar hukumar Wurno ta jihar Sokoto da tsakar dare, inda suka yi awon...

Yan bindiga sun kai hari a wani coci inda suka sace Fasto da matarsa da wasu masu ibada a jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da harin da aka kai wa Cocin Cherubim and Seraphim a garin Ejiba, karamar hukumar Yagba ya Yamma, da safiyar...

Mafi Shahara