DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kayan aikin dake filin jirgin saman Legas tsofaffi ne, akwai buƙatar yin gyara cikin gaggawa – Ganduje

-

 

Ganduje

Google search engine

Shugaban hukumar gudanarwa ta hukumar kula da filayen jiragen sama ta Nijeriya FAAN, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada bukatar gyara filin jirgin saman Legas na Murtala Muhammed cikin gaggawa saboda kayan aikin da ke filin jirgin saman sun tsufa.

Yayin ziyara ta farko da ya kai tare da rakiyar babbar daraktar hukumar ta FAAN, Olubunmi Kuku, Ganduje ya tabbatar da cewa yawancin kayan aikin filin jirgin sun lalace.

Ganduje ya kuma bayar da tabbacin cewa hukumar za ta hada kai da hukumomi domin inganta filayen jirgin sama ta yadda za su yi gogayya da na duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tankiya tsakanin Nijer da Benin ta sa kasashen rufe ofisoshin jakadancin juna

Kasashen Benin da Niger sun kori jami’an diflomasiyyar juna a wani mataki na ramuwar gayya, bayan shafe kusan shekara biyu ana takun-saka a tsakaninsu, a...

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutane fiye da 30 a jihar Neja

Aƙalla mutane 30, ciki har da mata, sun rasu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari Kasuwan Daji da ke ƙauyen Demo, Borgu LGA a...

Mafi Shahara