DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kayan aikin dake filin jirgin saman Legas tsofaffi ne, akwai buƙatar yin gyara cikin gaggawa – Ganduje

-

 

Ganduje

Google search engine

Shugaban hukumar gudanarwa ta hukumar kula da filayen jiragen sama ta Nijeriya FAAN, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada bukatar gyara filin jirgin saman Legas na Murtala Muhammed cikin gaggawa saboda kayan aikin da ke filin jirgin saman sun tsufa.

Yayin ziyara ta farko da ya kai tare da rakiyar babbar daraktar hukumar ta FAAN, Olubunmi Kuku, Ganduje ya tabbatar da cewa yawancin kayan aikin filin jirgin sun lalace.

Ganduje ya kuma bayar da tabbacin cewa hukumar za ta hada kai da hukumomi domin inganta filayen jirgin sama ta yadda za su yi gogayya da na duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Alƙali ya yi barazanar soke belin Abdulrasheed Maina da ake zargin kan zambar N738.6m

Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke Abuja, ta yi barazanar soke belin tsohon shugaban kwamitin garambawul a harkar fansho na ƙasa, Abdulrasheed Maina,...

Majalisar dattawa ta musanta ƙin amincewa da aika sakamakon zaɓe ta na’ura

Bangaren ’yan adawa a Majalisar Dattawan Nijeriya ya fayyace a ranar Alhamis cewa Majalisar ba ta ƙi amfani da tsarin tura sakamakon zaɓe ta na’ura...

Mafi Shahara