DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NDLEA ta lalata tan 25 na miyagun kwayoyi a Kogi

-

NDLEA 

Hukumar hana da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya NDLEA reshen jihar Kogi ta lalata tan 25 na miyagun kwayoyi a Lokoja babban birnin jihar a ranar Laraba.

Google search engine

Wakilin shugaban hukumar NDLEA Brig. Janar Mohammed Buba Marwa a wajen taron, daraktan ayyuka da bincike na hukumar ta NDLEA, Ahmed Suleiman Ningi, ya jaddada illar da ke tattare da irin wadannan haramtattun magunguna.

Ya ce idan aka bari mutane na amfani da haramtattun magunguna irin haka,yana iya kara tsananta kalubalen tsaro a cikin kasar.

Kwayoyin da aka lalata sun hada da, Tramadol, Rohypnol, Diazepam, Exol-5, Pentazocine da  Cocaine.

Kwamandan hukumar NDLEA na jihar Kogi, Umah Mustapha Yahuza, ya bayyana cewa an kama motoci 24 na masu safarar miyagun kwayoyi tare da kwacesu. 

Ya bukaci hadin kan al’umma wajen yaki da fataucin miyagun kwayoyi, ya kuma bayyana cewa akwai karin tan biyar na haramtattun kwayoyi har yanzu ana ci gaba da shari’a akai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ka fito ka bayyana wa ‘yan Nijeriya hakikanin dalilin da ya sa ka canza hafsoshin tsaro – Bukatar ADC ga shugaba Tinubu

Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana gaskiya ga ’yan Nijeriya kan ainihin dalilan da suka sa aka yi gaggawar sauya shugabannin...

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya nada yayansa a matsayin Sarkin Duguri

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya naɗa yayansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sarkin sabon masarautar Duguri da aka ƙirƙira a jihar. Sakataren gwamnatin Jiha, Aminu...

Mafi Shahara