DCL Hausa Radio
Kaitsaye

A janye dakatarwar da aka yi ma Natasha ko kuma mu makaka kotu- SERAP ga Akpabio

-

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci a Nijeriya ta yi kira da babbar murya ga shugaban majalisar dattawan Nijeriya Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalissa ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Kungiyar ta bayyana matakin dakatarwar a matsayin rashin bin doka da kuma take ma mata ‘yancin fadar albarkacin baki.

Google search engine

Wannan dai na a cikin wata budaddiyar wasika mai dauke da kwanan wata na 8 ga watan Maris 2025, wanda mataimakin daraktan kungiyar ta SERAP, Kolawole Oluwadare ya sa ma hannu, SERAP ta yi gargadin cewa za ta yi shari’a idan har shugaban majalisar dattawa ya ki bin gargadin cikin sa’o’i 48.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara