DCL Hausa Radio
Kaitsaye

A janye dakatarwar da aka yi ma Natasha ko kuma mu makaka kotu- SERAP ga Akpabio

-

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci a Nijeriya ta yi kira da babbar murya ga shugaban majalisar dattawan Nijeriya Godswill Akpabio da ya gaggauta janye dakatarwar da majalissa ta yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Kungiyar ta bayyana matakin dakatarwar a matsayin rashin bin doka da kuma take ma mata ‘yancin fadar albarkacin baki.

Wannan dai na a cikin wata budaddiyar wasika mai dauke da kwanan wata na 8 ga watan Maris 2025, wanda mataimakin daraktan kungiyar ta SERAP, Kolawole Oluwadare ya sa ma hannu, SERAP ta yi gargadin cewa za ta yi shari’a idan har shugaban majalisar dattawa ya ki bin gargadin cikin sa’o’i 48.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara