DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar NNPP a Nijeriya ta bukaci El-Rufai ya nemi afuwarta bisa zargin da ya yi mata

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna 

Jam’iyyar NNPP ta kasa ta yi Allah-wadai bisa zargin da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya yi wa jam’iyyar cewa gwamnatin tarayya ce ta dauki nauyinta dangane da korar tsohon dan takararta na shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso da kuma dakatar da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.

Sakataren jam’iyyar na kasa, Oginni Olaposi, ne ya yi wannan Allah-Wadai ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Ta cikin sanarwar NNPP ta zargi El-Rufai, da kokarin kawar da hankalin mutane daga ainihin abubuwan da ke faruwa yanzu haka.

Tsohon gwamnan na Kaduna wanda a baya-bayan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ce ke rura wutar rikicin jam’iyya mai mulki da kuma na jam’iyyun adawar kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnonin Benue da Zamfara da shugabannin majalisunsu su wa’adin mako daya su gaggauta bayyana a gaban kwamitinta

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, da na jihar Zamfara, Dauda Lawal, tare da shugabannin majalisun dokokin jihunsu wa’adin mako guda...

Mafi Shahara