DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar NNPP a Nijeriya ta bukaci El-Rufai ya nemi afuwarta bisa zargin da ya yi mata

-

Tsohon gwamnan jihar Kaduna 

Google search engine

Jam’iyyar NNPP ta kasa ta yi Allah-wadai bisa zargin da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya yi wa jam’iyyar cewa gwamnatin tarayya ce ta dauki nauyinta dangane da korar tsohon dan takararta na shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso da kuma dakatar da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.

Sakataren jam’iyyar na kasa, Oginni Olaposi, ne ya yi wannan Allah-Wadai ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Ta cikin sanarwar NNPP ta zargi El-Rufai, da kokarin kawar da hankalin mutane daga ainihin abubuwan da ke faruwa yanzu haka.

Tsohon gwamnan na Kaduna wanda a baya-bayan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa SDP, ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ce ke rura wutar rikicin jam’iyya mai mulki da kuma na jam’iyyun adawar kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara