DCL Hausa Radio
Kaitsaye

El-Rufai ya musanta zargin cin amanar Atiku, ya kuma bukaci Peter Obi, Aregbesola, da su shiga jam’iyyar SDP

-

Malam Nasir El-Rufa’i

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya musanta zargin cin amanar tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar.

Da yake magana a wata hira da BBC Hausa,El-Rufai wanda ya fice daga jam’iyyar APC zuwa SDP,cikin makon da ya gabata, ya bukaci shugabannin adawa da suka hada da Atiku Abubakar, Peter Obi na Labour Party, tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi, da Rauf Aregbesola, da su koma jam’iyyar SDP.

Da yake bayyana rashin jin dadinsa da gwamnati mai ci, El-Rufai, ya bayyana takaicinsa bisa yadda suka goyi bayan shugaba Tinubu da nufin kawo ci gaba domin sunga yadda ya kai wa Legas ci gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara