DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Ilimi Tunji Alausa, ya bukaci majalisar dokokin Nijeriya ta dakatar da aiki kan kudirin kafa sabbin jami’o’i

-

Tunji Alausa

Ministan Ilimi Tunji Alausa, ya bukaci majalisar dokokin Nijeriya ta dakatar da aiki kan kudirin kafa sabbin jami’o’i

Da yake jawabi a wajen taron manema lanarai na ministoci da aka yi a Abuja, Tunji Alausa ya koka da yadda jami’o’i ke kara yawa yayin da wadanda ake da su ke fama da kalubalen kudade.

Google search engine

Ministan ya yi kira ga ‘yan majalisar tarayyar, da su dakatar da kudurin kafa sabbin jami’oin domin suna cin kudade da yawa, inda ya ce zuwa yanzu akwai kudirori kusan 200 a gaban majalisar dokokin kasar na kirkiro sabbin jami’o’i, kuma wadanda ake da su babu isassun kayan aikin tafiyar da su.

Don haka ya bukaci maimakon kafa sabbin makarantu, kamata ya yi a inganta wadanda ake da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara