DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amnesty ta yi Alla-wadai da tsare ‘yan jarida biyu a Kano bisa umurnin kwamishinan Abba Gida-Gida

-

 

Google search engine

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International a Nijeriya, ta yi Alla-wadai kan cin zarafi da kama wasu ‘yan jarida da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta yi bisa umurnin kwamishinan yada labarai Ibrahim Waiya, a cewar kungiyar mai kare hakkin dan Adam a kasashen duniya.

Kungiyar na zargin kwamishinan ya ba da umurnin kama Buhari Abba Rano, mawallafin jaridar yanar gizo ta Kano Times da Isma’il Auwal, dan jarida mai zaman kansa, saboda wallafa wani ra’ayi da suka yi.

Amnesty International ta bukaci gwamnatin jihar Kano da rundunar ‘yan sanda su kare hakkin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin wadannan ‘yan jarida gami da dakatar da yunkurin gurfanar da yan jaridar gaban kotu da zargin yunkurin bata suna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara