DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zauren matasan Arewacin Nijeriya ya yi fatali da kudirin samar da sabbin kananan hukumomi 37 a jihar Legas

-

Zauren matasan Arewacin Nijeriya 

Zauren matasan Arewacin Nijeriya NYCN ya yi watsi da kudurin da aka gabatar na kara sabbin kananan hukumomi 37 a jihar Legas.

Shugaban zauren NYCN na kasa, Isah Abubakar, ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya bayyana kudurin da aka gabatar a matsayin rashin adalci da kuma barazana ga hadin kan kasa.

Google search engine

A Larabar da ta gabata ne dai majalisar wakilan Nijeriya ta yi karatu na biyu kan kudurin da ke neman karin ƙananan hukumomin daga 20 zuwa 57, wanda hakan ke nuna cewa adadin kananan hukumomin kasar zai karu daga 774 zuwa 811.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara