DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ECOWAS za ta yi zama kan harajin da kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar

-

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS za ta gudanar da taro a cikin watan Afrilun da muke domin tattaunawa kan harajin kashi 0.5 cikin 100 na shigo da kaya da kasashen yankin Sahel suka ƙaƙaba wa ƙasashen kungiyar ECOWAS a baya-bayan.
Shugaban sashen yaɗa labarai na Hukumar ECOWAS Joel Ahofodji, ya tabbatar da cewa majalisar kungiyar za ta yi taro a ranar 22 ga Afrilu don tattaunawa kan lamarin da sauran batutuwan da suka shafi kasashen, a cewar jaridar Dailytrust.
Da aka tambaye shi ko ECOWAS za ta dauki wani mataki na ramuwa dangane da harajin kashi 0.5 da AES suka sanya, Joel Ahofodji ya bayyana cewa, kungiyar za ta tattauna kan matakin da zata dauka a lokacin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara