DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fadar shugaban kasa ta ƙaryata zargin aikata ba daidai ba wajen ba da mukaman gwamnati kamar yadda ake yaɗawa

-

A cikin wata sanarwa da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (OSGF) ya fitar, gwamnatin ta ce tana bin tanadin kundin tsarin mulkin kasa na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwanskwarima) musamman sashen 14, wajen tabbatar da adalci da wakilci daga dukkan yankuna.
Sanarwar ta ce Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, na da cikakken burin hadin kan kasa, kuma yana yin nade-nade ne bisa tushen gaskiya, adalci da ga kowa da kowa.
Ofishin sakataren gwamnatin ya bukaci jama’a da su yi watsi da jita-jitar da ba su da tushe, tare da shawartar su da su dinga dogaro da hanyoyin sadarwa na hukuma wajen samun sahihan bayanai.
A karshe, sanarwar ta gargadi masu yada kalaman rarrabuwar kai da zargin da ba su da tabbas da su daina, domin hakan ba zai amfani kasar nan ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin...

Jam’iyyar APC ta kalubalanci Gwamnan Filato Mutfwang da ya bayyana masu matsa masa lamba ya bar PDP

Jam’iyyar APC ta jihar Filato ta kalubalanci Gwamna Caleb Mutfwang da ya fito fili ya bayyana sunayen mutanen da ke matsa masa lamba ya bar...

Mafi Shahara