DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban mulkin sojin Gabon ya lashe zaben da aka gudanar

-

Shugaban mulkin sojin kasar Gabon, Brice Oligui Nguema, ya lashe zaben shugaban kasar, bisa ga sakamakon da aka fara fitarwa na wucin-gadi.
Sakamakon farko da aka sanar a ranar Lahadi ya nuna cewa Nguema, wanda ya jagoranci juyin mulkin soja a shekarar 2023, ya samu kusan kashi 80% na kuri’un da aka kada.
A bisa kashi 90.35% na kuri’un da aka kidaya, abokin hamayyarsa mafi kusa, Alain-Claude Bilie-By-Nze, ya samu kusan kashi 3% yayin da sauran ’yan takara shida ba su samu fiye da kashi 1% ba, in ji Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta kasar.
Nguema, wanda ya ba da gudunmuwa matuka wajen kawo karshen shekaru 55 na mulkin mallaka karkashin iyalan Bongo da tsohon shugaban kasa Ali Bongo ke jagoranta, an dade ana kyautata zaton zai lashe zaben ranar Asabar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara