DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

-

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa jam’iyyar APC, a matsayin abin takaici da kuma raɗaɗi.

Damagum ya bayyana haka ne a wani biki da aka gudanar a Abuja domin mika takardar shaidar nasara ga Jude Ezenwafor, wanda jam’iyyar PDP ta tsayar a matsayin ɗan takarar gwamna a Zaben jihar Anambra dake tafe, inda yace shugabancin jam’iyyar na PDP yana yin nazari domin kafa kwamitin rikon ƙwarya a jihar Delta.

Google search engine

Damagum ya ce babban zaɓen shekarar 2027 ba zai ta’allaka ga yawan gwamnoni da kowace jam’iyya ke da su ba, ya kuma yi kira ga dukkan ‘ya’yan jam’iyyar da su ɗaure damara, su haɗa kai domin ceton Najeriya, yana mai jaddada cewa babu wani ƙalubale da ba za su tunkara ba.

Gwamna Oborevwori da wanda ya gaji, tsohon Gwamna Ifeanyi Okowa, tare da wasu jiga-jigan PDP a jihar, sun sauya sheƙa zuwa APC a ranar Laraba, lamarin da ya kawo ƙarshen jita-jitar da ta dade tana yawo a jihar.

Tun daga farkon mulkin dimokuraɗiyya a shekarar 1999, jam’iyyar PDP ce ke jan ragamar mulki a jihar ta Delta dake da arzikin man fetur a shiyyar kudu maso kudancin Najeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara