DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

-

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga cikin kasashen da Allah ya hore da albarkatun kasa.

Wannan na cikin rahoton Africa Pulse da aka fitar yayin taron asusun bada lamuni na duniya IMF da Bankin Duniya da ke gudana a birnin Washington D.C na Amurka.

Rahoton ya nuna cewa yankin Afrika ta Kudu da kasashen yankin Sahel (Sub-Saharan Africa) na da mafi yawan talakawa a duniya, inda kusan kaso 80 cikin 100 na talakawan duniya ke zaune a wannan yanki.

Najeriya na daga cikin kasashe hudu da ke dauke da rabin yawan talakawan da suka kai miliyan 560 a Afrika.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara