DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Abuja Nyesom Wike ya ba da umarnin rufe asibitocin da aka yisu ba bisa ka’ida ba

-

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ba da umurnin rufe duk wani asibitin da ba a yi wa rajista ba da kuma ma’aikatan jinya da ke aiki a babban birnin tarayya Abuja.

Babban mataimaki na musamman ga ministan kan harkokin yada labarai Olayinka ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Asabar.

Google search engine

Olayinka ya bayyana cewa ministan ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake magana kan mutuwar wata mata mai juna biyu a wani asibiti mai zaman kansa da ke Durumi, Abuja, bayan tiyatar da aka yi mata.

A cewarsa, ministan ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu yana gudanar da aikin ta haramtacciyar hanya ko kuma yana aiki a wani asibiti da bashi da rajista to a kama shi kuma a hukunta shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban kasar Djibouti zai sake tsayawa takara karo na shida

Shugaban ƙasar Djibouti mai shekaru 77, Ismail Omar Guelleh zai sake tsayawa takara karo na shida Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh, wanda yake mulki tun...

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambara ya zargi jam’iyyar APGA da sayen kuri’u

Dan takarar ADC a zaben gwamnan Anambra, John Nwosu, ya zargi jam’iyyar APGA da sayan da kuri’a a zaben da yake ci-gaba da gudana a...

Mafi Shahara