DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

-

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya.

Google search engine

Bafarawa, wanda ya kasance jigo a jam’iyyar babbar jam’iyyar adawa ta PDP har zuwa ranar 13 ga Janairun 2025, ya sanar da murabus dinsa daga jam’iyyar, yana mai bayyana cewa yana son mayar da hankali kan shirye-shiryen bunkasa matasa.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, tsohon gwamnan jihar Sokoto ya ce ’yan siyasar Najeriya sun fi mayar da hankali ne wajen samun mukaman siyasa ba tare da yin wani abu na amfani ga al’umma ba.

Bafarawa ya yi wannan jawabi ne a yayin da wasu fitattun ’yan adawa ke sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, a shirye-shiryen da ake yi gabanin zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban hafsan sojin kasa ya umurci sojoji da su tsaurara wajen ganin sun ceto dalibai mata da aka sace a jihar Kebbi

Babban hafsan rundunar sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun Operation Fansan Yamma da su matsa kaimi wajen ceto daliban GGCSS Maga da...

’Yan bindiga sun sace fasinjoji shida a hanyar Ogobia–Adoka a Benue

’Yan bindiga sun tare wata motar haya suka tafi da fasinjoji shida sannan suka kashe direba a hanyar Ogobia–Adoka da ke ƙaramar hukumar Otukpo a...

Mafi Shahara