Majalisar kungiyar kasashen yammacin Africa wato ECOWAS ta yi kira ga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar da su sake nazari kan matakin ficewar cikin kungiyar.
A karshen wani taro na kwanaki biyar da majalisar ta yi a birnin Banjul na kasar Gambia, shugaban kwamitin hadin gwiwa Sanata Edwin Melvin Snowe Jr., ya jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin kasashen da ke yankin.
Sanata Edwin ya bayyana ficewar kasashen uku a matsayin wani abu da ya yi wa kasashen zafi, yana mai cewa kungiyar ta kasance a haɗe tsawon shekaru hamsin da suka gabata sai yanzu da kasashen suka fice.
Kasashe uku na yankin Sahel wadanda sojojin da suka yi juyin mulki ke jagoranta a yanzu, sun sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS ne a ranar 28 ga watan Junairu, 2024, kuma ficewar ta fara aiki ne a watan Janairun 2025.