DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ECOWAS ta yi kira ga Nijar, Mali da Burkina Faso su sake shiga kungiyar

-

Majalisar kungiyar kasashen yammacin Africa wato ECOWAS ta yi kira ga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar da su sake nazari kan matakin ficewar cikin kungiyar.

A karshen wani taro na kwanaki biyar da majalisar ta yi a birnin Banjul na kasar Gambia, shugaban kwamitin hadin gwiwa Sanata Edwin Melvin Snowe Jr., ya jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin kasashen da ke yankin.

Sanata Edwin ya bayyana ficewar kasashen uku a matsayin wani abu da ya yi wa kasashen zafi, yana mai cewa kungiyar ta kasance a haɗe tsawon shekaru hamsin da suka gabata sai yanzu da kasashen suka fice.

Kasashe uku na yankin Sahel wadanda sojojin da suka yi juyin mulki ke jagoranta a yanzu, sun sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS ne a ranar 28 ga watan Junairu, 2024, kuma ficewar ta fara aiki ne a watan Janairun 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara