DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bukola Saraki zai jagoranci sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar PDP

-

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP tare da tsoffin gwamnonin jam’iyyar sun nada tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Bukola Saraki, a matsayin shugaban kwamitin sulhu mai mambobi bakwai.

Shugaban kungiyar Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai bayan wani muhimmin taro da suka yi da tsoffin gwamnonin jam’iyyar a Abuja.

Google search engine

Gwamna Bala Mohammed ya ce an dora wa wannan kwamiti mai mutane bakwai nauyin sasanta mambobin jam’iyyar da ke cikin sabani kafin babban taron kwamitin zartaswa na kasa NEC na jam’iyyar PDP da aka shirya gudanarwa a ranar 27 ga Mayu, da kuma babban taron jam’iyyar na kasa da ke tafe a watan Agusta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara