DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bukola Saraki zai jagoranci sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar PDP

-

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP tare da tsoffin gwamnonin jam’iyyar sun nada tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya Bukola Saraki, a matsayin shugaban kwamitin sulhu mai mambobi bakwai.

Shugaban kungiyar Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai bayan wani muhimmin taro da suka yi da tsoffin gwamnonin jam’iyyar a Abuja.

Google search engine

Gwamna Bala Mohammed ya ce an dora wa wannan kwamiti mai mutane bakwai nauyin sasanta mambobin jam’iyyar da ke cikin sabani kafin babban taron kwamitin zartaswa na kasa NEC na jam’iyyar PDP da aka shirya gudanarwa a ranar 27 ga Mayu, da kuma babban taron jam’iyyar na kasa da ke tafe a watan Agusta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Murabus din Ganduje wata maƙarƙashiya ce aka shirya domin cire Shettima daga gwamnatin Tinubu – Zargin wasu mutanen Borno

Wasu daga cikin al'ummar jihar Borno sun zargi murabus din Ganduje a matsayin wata maƙarƙashiya da aka shirya domin a kawar da Kassim Shettima a...

Mafi Shahara