DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata budurwa ta sace kanta, ta nemi a biya kudin fansa Naira milyan 2

-

Wata budurwa, dalibar sakandare mai kimanin shekaru 16, ta shirya karyar sace kanta tare da neman a biya kudin fansa har Naira milyan biyu don a sako ta.

Dalibar ‘yar ajin SS2 a wata makarantar sakandare mai zaman kanta da ke birnin Abakaliki na jihar Ebonyi ta tuntubi wani dan’uwa daga cikin iyalansu, inda ta yi ikirarin cewa an sace ta.

Google search engine

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Joshua Ukandu, ya shaida wa manema labarai cewa wani makusancinta ne ya taimaka mata wajen shirya wannan karyar.

Sai dai ‘yan sandan ba su ambaci sunan dalibar ba da makarantar da take karatu.

‘Yan sandan dai sun ce har yanzu suna bincike kan wannan lamari domin tabbatar da hakikanin abin da ya faru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara