DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kudurin dokar tilasta yin zabe ga kowane dan Nijeriya ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai

-

By Salim Muhammad Musa

Kudurin na gyaran dokar zabe ta shekara ta 2022, ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai a wannan Alhamis.

Google search engine

Idan har wani kudurin da ke gaban majalisa ya zama doka, za a tilasta wa kowane dan Nijeriya da shekarunsa suka kai na yin zabe, fita ya jefa kuri’arsa a rumfar zabe.

Kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas, da kuma dan majalisa Daniel Ago ne suka dauki nauyin gabatar da wannan kudurin a zauren majalisa, a cewar jaridar Punch.

Daniel Ago ya bayyana cewa idan aka amince da wannan gyaran, zai magance dabi’ar nan ta kin yin zabe da wasu ‘yan kasa ke yi a lokacin da sauran yan uwansu ke can kan layi domin kada kuri’a.

Haka kuma ya ce dokar za ta ƙarfafa wa ‘ƴan ƙasa shiga tsarin zaɓe domin a dama da su wajen zaben shugabanni.

Duk da cewa ƙudirin ya tsallake karatun na biyu, dan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP daga jihar Akwa Ibom, Mark Esset, ya ce yin doka kawai ba zai kawo chanji ga tsarin zaben kasar ba.

A cewar dan majalisar, mafi yawan ‘yan Nijeriya sun cire tsammani akan tsarin zaben kuma suna ganin cewa kuri’unsu ba sa da muhimmanci, shi ya sa ba sa fita su kada kuri’arsu a lokacin zabe.

Mark Esset ya ce idan har ana son wannan dokar ta yi aiki, to dole ne a tabbatar da cewa kuri’ar kowane dan kasa tana da tasiri a zabe.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara