DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ruwan sama da iska mai karfi ya rusa gidan wasu sabbin ma’aurata a Katsina

-

Akalla gidaje 300 ne suka rushe, tare da asarar dukiyoyi da darajarsu ta haura miliyoyin Naira, sakamakon wani hadari mai karfi tare iska da aka samu tare da ruwan sama a wasu unguwanni a birnin Katsina.

Lamarin da ya dauki kusan mintuna goma sha biyar da yamma bayan sallar La’asar a ranar Laraba, ya haddasa kwarewar rufin gine-gine kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.

Google search engine

Daga cikin wuraren da lamarin ya fi shafa akwai Sabuwar Unguwar Modoji, Shinkafi, da yankin Kukar-Gesa, har da Ambassador Quarters da kuma wasu sassan karamar hukumar Jibia.

Mutane da dama, ciki har da wasu sabbin ma’aurata, sun rasa matsugunansu sakamakon wannan iftila’i.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaro a Abuja

Taron, wanda ya gudana kwanaki uku bayan sanar da sabbin nade-naden, shi ne karo na farko da shugaban kasa ya gana da manyan hafsoshin rundunonin...

Paul Biya ya yi wa masu zanga-zangar sakamakon zabe shagube a Kamaru

Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya yi shagube ga rikicin siyasar da ke faruwa bayan ayyana shi a matsayin wanda ya lashe sakamakon zaɓen shugaban...

Mafi Shahara