DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Flying Eagles ta sha kashi a hannun Afrika ta Kudu da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na AFCON U-20

-

Kasar Afirka ta Kudu ta doke ‘yan wasan Flying Eagles na Nijeriya da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika na ‘yan kasa da shekaru 20.

An buga wasan ne a filin wasa na Suez Canal ranar Alhamis, don samun tikitin zuwa wasan karshe na gasar AFCON ta ‘yan kasa da shekaru 20 a kasar Masar.

Nasarar ta ba Afirka ta Kudu damar kaiwa wasan karshe na AFCON U-20 karo na biyu a tarihin ta, karon farko tun 1997, lokacin da suka kare a matsayin na biyu.

Ga Nijeriya kuwa, wannan shi ne karo na uku a jere da ta sha kaye a matakin wasan kusa da na karshe, bayan da Gambiya ta doke ta a shekarar 2023 da Mali a 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara