DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Flying Eagles ta sha kashi a hannun Afrika ta Kudu da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na AFCON U-20

-

Kasar Afirka ta Kudu ta doke ‘yan wasan Flying Eagles na Nijeriya da ci 1-0 a wasan dab da na karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika na ‘yan kasa da shekaru 20.

An buga wasan ne a filin wasa na Suez Canal ranar Alhamis, don samun tikitin zuwa wasan karshe na gasar AFCON ta ‘yan kasa da shekaru 20 a kasar Masar.

Google search engine

Nasarar ta ba Afirka ta Kudu damar kaiwa wasan karshe na AFCON U-20 karo na biyu a tarihin ta, karon farko tun 1997, lokacin da suka kare a matsayin na biyu.

Ga Nijeriya kuwa, wannan shi ne karo na uku a jere da ta sha kaye a matakin wasan kusa da na karshe, bayan da Gambiya ta doke ta a shekarar 2023 da Mali a 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara