DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami’an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta.

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa zaman lafiyar dimokradiyyar Nijeriya, daidaiton yankin da ci gaban tattalin arziki na da alaka kai tsaye da tsaron kasa, inda ya umurci a dauki matakin karshe kan duk wasu abokan gaba da ke barazana ga zaman lafiyar kasar.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja, a yayin bikin karbar sabbin jiragen sama guda biyu samfurin Agusta 109 Trekker, wanda aka shirya a matsayin wani bangare na bukukuwan cika shekaru 61 da kafuwar Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya.

Shugaban, wanda Mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta, ya jaddada cewa dole ne a karfafa tsaron kasa domin al’ummar Nijeriya su samu damar gudanar da ayyuka masu amfani da kuma habbaka tattalin arzikin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara