DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro sun kama wani mai garkuwa da mutane yana shirin tafiya aikin hajji a Abuja

-

Jami’an tsaro sun kama wani da ake nema ruwa a jallo bisa laifin garkuwa da mutane a sansanin aikin hajji da ke Abuja.

Wata majiya daga cikin jami’an tsaro da ke aiki a sansanin ta tabbatar wa da jaridar Daily Trust kama wanda ake zargin, a ranar Lahadi.

Majiyar ta ce an cafke wanda ake zargin ne yayin tantance mahajjatan da ke shirin tashi zuwa Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana.

Majiyar ta bayyana cewa wanda ake zargin mai suna Yahaya Zango, mazaunin unguwar Paikon-Kore ne da ke karamar hukumar Gwagwalada a cikin babban birnin tarayya Abuja.

Jami’in tsaron ya ce hukumomin tsaro sun ayyana Yahaya a matsayin wanda ake nema, bisa zargin hannu da yake da shi a wasu laifukan garkuwa da mutane.

Ya kara da cewa wanda ake zargin ya gabatar da fasfonsa tare da sauran mahajjata daga Abuja da ke kan hanyarsu ta zuwa Saudiyya domin aikin hajji na bana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’an tsaron fadar Vatican sun hana Seyi Tinubu zuwa wurin Fafararoma a yayin bikin rantsar da shi

Jami'an Daily Trust ta ruwaito cewa a yayin ziyarar da Sheyin ya bi tawagar shugaba Tinubu, Bola Tinubu ya ganada da Peter Obi, daya daga cikin...

Trump zai gana da Putin ta wayar tarho kan tsagaita wuta a Ukraine

Shugaban Amurka Donald Trump zai tattauna ta wayar tarho da Vladimir Putin na Rasha a yau litinin a wani bangare na kokarin kawo karshen yakin...

Mafi Shahara