DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka yi hankali da ‘yan bani- na -iya a gwamnatin ka – Gargadin ‘yan Kwankwasiyya ga gwamnan Kano

-

Kungiyar Kwankwasiyya Coalition of Concern Citizens mai fafutuksr tabbatar da cigaba, ta gargadi Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano da, ya kula da ‘yan bani na iya a gwamnatinsa da ake kira “Cabals”

Wannan jan hankali na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar na kasa, Kwamared Dayyib Hassan Ahmad ya rabawa manema labarai.

A cewar sanarwar, hanyar da wasu ‘yan majalisar zartaswa suke gudanar da ayyukansu bai dace da kokarin gwamnan na ganin Kano da al’ummarta sun samu ci gaba ba.

Ya bayyana cewa kungiyar da aka kafa tun shekarar 2019 ta ga ya dace a ja hankalin gwamnan da ya yi taka-tsan-tsan da wasu daga cikin abokan aikinsa domin ba sa yin abinda ya kamata.

Sanarwar ta ce abin damuwa ne a ce an bar mutanen da suka yi kokari wajen ganin an samu nasarar jam’iyyar NNPP a Kano ba a kula da su ba, ya yi zarigin cewa wasu jiga-jigan gwamnatin ba su yi wani abin da ya taimaka wa gwamnatin Gwamna Abba ba, duk sun fito ne don neman biyan bukatun su ba wai yi wa al’umma aiki ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hadakar da nake sha’awa ita ce yaki da yunwa da Talauci a fadin Nijeriya

A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan...

Jami’an tsaron fadar Vatican sun hana Seyi Tinubu zuwa wurin Fafararoma a yayin bikin rantsar da shi

Jami'an Daily Trust ta ruwaito cewa a yayin ziyarar da Sheyin ya bi tawagar shugaba Tinubu, Bola Tinubu ya ganada da Peter Obi, daya daga cikin...

Mafi Shahara