DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta soke lasisin wasu gidajen gala 8 tare da haramta aikinsu a jihar

-

Shugaban hukumar tace fina-finai na jihar Kano Abba El-Mustapha, ya bayar da umurnin soke lasisin wasu gidajen gala takwas a jihar Kano tare da haramta aikinsu cikin gaggawa saboda saba ka’idojin hukumar.

Hakan ya fito ne a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar kuma ya rabawa manema labarai jim kadan bayan kammala taron gudanarwar hukumar.

Google search engine

A cewar sanarwar, gidajen gala 8 da abin ya shafa sun hada da.

1. Hamdala Entertainment (Ungoggo)

2. Lady J. Entertainment (Sanya Olu)

3. Dan Hausa Entertainment (Sanya Olu)

4. Ni’ima Entertainment (Zungeru)

5. Ariya Entertainment (Abedi Sabon Gari)

6. Babbangida Entertainment (Balatus)

7. Harsashi Entertainment (Ebedi Sabon Gari)

8. Wazobiya Entertainment (Sanya Olu)

Abdullahi Sani Sulaiman ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan rashin bin ka’idojin hukumar yasa aka dauki wannan mataki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

APC ba ta da juriyar ra’ayoyin jam’iyyun adawa – Rauf Aregbesola

Sakataren jam’iyyar ADC Ogbeni Rauf Aregbesola, ya zargi jam’iyyar APC mai mulki da rashin jurewa ra’ayoyin 'yan adawa da kuma amfani da ƙarfin gwamnati wajen...

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

Mafi Shahara