DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Saura kiris PDP ta daidaice, shi ya sa mambobinta ke tururuwar komawa APC – Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce jam’iyyar adawa ta PDP ta shiga zullumi da rashin tabbas sakamakon irin nasarorin da APC ke samu.

Da yake jawabi a taron kolin APC da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Ganduje ya ce APC za ta lashe zaben da ke tafe a babban birnin tarayya (FCT) saboda kwarewar siyasa da karfinta.

Google search engine

Ya ce rikice-rikice da sauya sheka da ke damun PDP ya sanya mambobinta da dama ke komawa APC.

Ganduje ya kara da cewa APC na da gwamnonin jihohi 22 daga cikin 36, kuma wani gwamna na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar.

Ya ce nasarorin APC a zabukan da suka biyo bayan na 2023 na nuna hasashen nasararta a 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara