DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An shiga takun-saka tsakanin wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC na jihar Plateau

-

Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC na yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya ta ba shugaban jam’iyyar APC na jihar Plateau Rufus Bature wa’adin kwanaki 7 ya kafa kwamitin sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar.

Kazalika, kungiyar ta kuma nemi bangaren Rufus da ya ba da dama ga sauran ‘yan wata jam’iyyar su shigo cikin APC a jihar don ciyar da jam’iyyar gaba.

Google search engine

Wannan wa’adi dai ya biyo bayan wani matakin kungiyar da dauko wani kyamfe na Green Cap Movement da ke nuna alamar yadda Gwamnan jihar na PDP Calep Mufwang yake saka hula.

Wannan kungiya dai ta dade tana kira ga Gwamnan jihar Calep Mutfwang da ya bar jam’iyyarsa ta PDP ya koma APC.

Shugaban kungiyar Saleh Abdullahi Zazzaga ya ce sun dauki wannan matakin ne domin kara jaddada kalamansu na mara baya ga tazarcen Shugaba Tinubu a zaben 2027.

Sai dai, a cikin wata sanarwa daga bangaren Rufus Bature, APC ta yi Allah-wadai da wannan shela ta Green Cap Movement da wannan kungiya ta dauko.

Sai dai, kungiyar North Central APC Forum ta zargi tsagin APC ta Rufus da yi wa wasu tsirarun mutane aiki ba don cigaban al’umma ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya tura bukatar sake cin bashin Dala Biliyan 21.5 da Naira Biliyan 758 ga majalisar dokoki

Majalisar dokokin Nijeriya ta ce ta karbi bukatar shugaban kasa Bola Tinubu ta neman sahalewa don cin rancen dala biliyan 21.5 daga waje da kuma...

An sa dokar biyan haraji ga duk wanda zai saurari rediyo cikin mota a kasar Zimbabwe

Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, ya rattaba hannu kan wata doka da za ta sa duk masu ababen hawa a kasar su sayi lasisin sanya...

Mafi Shahara