DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rikicin PDP ya kara rincabewa bayan da Wike ya janye daga kokarin sulhu da ake yi

-

Rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya kara kamari, yayin da ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya fice daga yarjejeniyar sulhu ta cikin gida da aka cimma a jam’iyyar adawa.

Wike ya zargi gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, kan matsalolin da suka dabaibaye jam’iyyar PDP, yana mai jaddada cewa shi ne ya jawo wannan matsalar.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, tsohon gwamnan na Rivers ya zargi shugabannin jam’iyyar da suka hada da gwamnan jihar Enugu, Peter Mbah da cin amana, da rashin gaskiya, da kuma take yarjejeniyar da aka yi da shi.

Ministan ya sha alwashin ci gaba da jan zare har sai ya samu adalci a jam’iyyar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Sau 22 ana yunkurin lalata mana matatar mai – Matatar man fetur ta Dangote

Kamfanin matatar mai ta Dangote ya bayyana cewa tun bayan da matatar man da ke fitar da ganga 650,000 a rana ta fara aiki, aƙalla...

Mafi Shahara