Shugaba Bola Tinubu ya jaddada kudurin gwamnatinsa na kare hakki tare da inganta jin dadin yara a Najeriya, wadanda ya ayyana a matsayin goben kasar.
A wani jawabi da ya fitar na bikin ranar yara ta 2025, Tinubu ya bayyana bukatar daukar matakin gaggawa don magance cin zali, da cin zarafin da yin watsi da ake yi w miliyoyin yara a fadin kasar.
Rahotanni sun nuna cewa kimanin kashi 65 cikin 100 na yaran da suka isa zuwa makaranta a Najeriya suna fuskantar wani nau’i na cin zarafi.
Akan wannan Shugaba Tinubu ya bayyana wasu tsare-tsare na kare yara da gwamnatin ta fito da su, da suka hada da inganta yanayin koyo, da tabbatar da cewa babu wani dan Najeriya da aka bari a baya.