DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya tura bukatar sake cin bashin Dala Biliyan 21.5 da Naira Biliyan 758 ga majalisar dokoki

-

Majalisar dokokin Nijeriya ta ce ta karbi bukatar shugaban kasa Bola Tinubu ta neman sahalewa don cin rancen dala biliyan 21.5 daga waje da kuma bashin Naira Biliyan 758 na cikin gida domin biyan fansho.

Bukatar shugaban wadda aka karanta a zauren majalisar dattawa yayin zaman majalisar na yau, na da nufin samar da kudade don samar da kayayyakin more rayuwa, inganta kiwon lafiya, ilimi, da samar da ruwan sha a kasar.

Google search engine

Majalisar ta mika bukatar ga kwamitin majalisar dattijai mai kula da basussukan cikin gida da waje don ya duba bukatar kuma ana sa ran zai gabatar da rahotonsa nan da makonni biyu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rashin tabbas da matsalolin tsaro na barazana ga burin ECOWAS na 2050 – Shugaban ECOWAS, Touray

Shugaban kungiyar ECOWAS, Omar Touray, ya ce rashin tabbas a duniya, matsalolin tsaro da matsin tattalin arziki na hana kungiyar cimma burinta na Vision 2050,...

An yi ajalin wata mace mai juna biyu da wani karamin yaro a cikin birnin Kano

Al’ummar Sheka Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kano Municipal sun shiga firgici a daren Asabar bayan wasu da ba a san ko su waye ba...

Mafi Shahara