DCL Hausa Radio
Kaitsaye

El-Rufai zai biya diyyar Naira miliyan 900 kan tsare dattawan kabilar Adara ba bisa ka’ida ba a 2019

-

Kotun tarayya da ke Kaduna ta yanke hukunci kan tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, da wasu mutum biyar, inda ta umarce su su biya Naira miliyan 900 a matsayin diyyar kame da tsare wasu dattawan Adara ba bisa ka’ida ba a 2019.

Mai shari’a Hauwa’u Buhari ce ta yanke hukuncin, tana mai cewa an kama dattawan tara, ciki har da tsohon kwamishina da dan sanda mai ritaya, bisa zargin hannu a kisan sarkin gargajiyar su, Raphael Maiwada Galadima.

Google search engine

An kama su ne bisa umarnin El-Rufai a matsayinsa na dan kasa, ba a matsayin gwamna ba kamar yadda rahoton gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara