Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta roki Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya da ta sake buɗe Ƙofar neman biza domin bai wa sauran ‘yan Najeriya damar kammala shirin hajjin 2025.
A wata wasiƙa da ta aike ranar 24 ga Mayu, NAHCON ta bayyana buƙatar a matsayin ta ujila don taimaka wa waɗanda ke cikin rudani samun damar zuwa su sauke farali.
Wannan roƙon ya biyo bayan sanarwar cibiyar Nusuk ta Saudiyya da ta tabbatar da rufe ƙofar bayar da biza, wanda aka fara ware wa har zuwa 29 ga Afrilu, sai aka tsawaita bayan matsin lamba daga shugaban Pakistan.
Ko da yake rufewar ta shafi duk ƙasashen da ke halartar hajji, NAHCON na ƙoƙarin ganin an bai wa Najeriya ƙarin dama, yayin da har yanzu hukumomin Saudiyya ba su ce uffan ba game da lamarin.



