DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya ba da umurnin buɗe cibiyar agajin gaggawa a Neja saboda ambaliyar Mokwa

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin a gaggauta bude cibiyar bayar da agajin gaggawa ta kasa a jihar Neja, biyo bayan mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a karamar hukumar Mokwa ta jihar.

Shugaban ya bayar da wannan umarni ne da sanyin safiyar Asabar bayan da rahotanni suka nuna cewa ambaliyar ta yi sanadin asarar rayuka sama da 100 tare da raba iyalai da dama.

Google search engine

A wata sanarwa da ya fitar a shafin sa na X, Shugaba Tinubu ya yi jimamin faruwar ibtila’in, ya kuma yi alkawarin daukar matakin gaggawa da tura agajin jin kai na gwamnatin tarayya don tallafa wa al’ummomin da abin ya shafa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara