DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya ba da umurnin buɗe cibiyar agajin gaggawa a Neja saboda ambaliyar Mokwa

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin a gaggauta bude cibiyar bayar da agajin gaggawa ta kasa a jihar Neja, biyo bayan mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a karamar hukumar Mokwa ta jihar.

Shugaban ya bayar da wannan umarni ne da sanyin safiyar Asabar bayan da rahotanni suka nuna cewa ambaliyar ta yi sanadin asarar rayuka sama da 100 tare da raba iyalai da dama.

Google search engine

A wata sanarwa da ya fitar a shafin sa na X, Shugaba Tinubu ya yi jimamin faruwar ibtila’in, ya kuma yi alkawarin daukar matakin gaggawa da tura agajin jin kai na gwamnatin tarayya don tallafa wa al’ummomin da abin ya shafa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili shi ne Mataimakin Editan Gudanarwa kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki na DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin tabbatar da inshorar lafiya a dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnatin Nijeriya

Shugaba Bola Tinubu ya umarci sakataren gwamnatin tarayya da ya fitar da takardar umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomi domin tabbatar da inshorar lafiya bisa...

Zan iya kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga cikin watanni biyu muddin na samu iko da hukumomin tsaro – Gwamnan Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa matsalar ayyukan ’yan bindiga da ke addabar jihar za ta zama tarihi muddin ya samu damar bayar da...

Mafi Shahara