DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani magidanci ya yanke jiki ya fadi saboda jin matarsa ta haifi ‘yan uku a Kogi

-

Wani magidanci mai suna Adamu Muhammed Tenimu ya fadi ya suma a asibitin koyarwa ta jami’ar tarayya dake Lokoja a jihar Kogi, bayan samun labarin cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya uku.

Shaidun gani da ido sun ce mutumin da ya ji cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya uku, dukkansu ‘yan mata, sai ya fada shauki kuma nan take aka ga ya fadi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Jami’an asibitin sun yi gaggawar kai masa agaji, bayan ya farfado aka sanar da shi uwar da ‘ya’yanta uku suna cikin koshin lafiya.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan farfaɗowa, Muhammed ya bayyana cewa farin ciki da tunanin rashin iya daukar nauyin da ya rataya a wuyansa na kula da yaran, shine ya sa ya yanke jiki ya fadi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Mafi Shahara