Wani magidanci mai suna Adamu Muhammed Tenimu ya fadi ya suma a asibitin koyarwa ta jami’ar tarayya dake Lokoja a jihar Kogi, bayan samun labarin cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya uku.
Shaidun gani da ido sun ce mutumin da ya ji cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya uku, dukkansu ‘yan mata, sai ya fada shauki kuma nan take aka ga ya fadi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Jami’an asibitin sun yi gaggawar kai masa agaji, bayan ya farfado aka sanar da shi uwar da ‘ya’yanta uku suna cikin koshin lafiya.
Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan farfaɗowa, Muhammed ya bayyana cewa farin ciki da tunanin rashin iya daukar nauyin da ya rataya a wuyansa na kula da yaran, shine ya sa ya yanke jiki ya fadi.



