Chibudom Nwuche, tsohon mataimakin shugaban majalisar wakilan Nijeriya daga shekarar 1999 zuwa 2003, ya ce babban birnin tarayya na kan hanyarsa ta zama cikin biranen duniya mafi kayatarwa a karkashin shugabancin Shugaba Bola Tinubu da Minista Nyesom Wike.
Mista Nwuche ya bayyana haka ne a Abuja, lokacin da ya raka ministan babban birnin tarayya ziyarar duba ayyukan da ake gudanarwa a cikin birnin, a shirye-shiryen kaddamar da bikin cika shekaru biyu na shugaban kasa Bola Tinubu.
Wasu daga cikin ayyukan sun hada da titin Kasuwa da Fada da aka kammala a Gwagwalada, sai titi mai nisan kilomita 15 da ya tashi daga A2 zuwa Pai da kuma na Pai zuwa Gumani mai tsawon kilomita 15.4 a karamar hukumar Kwali.



