DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 30 a gabascin Indiya

-

Mamakon ruwan sama na tsawon kwanaki biyu ya haddasa ambaliyar ruwa da zabtarewar kasa tare da yin sanadin mutuwar mutane akalla 30 a arewa maso gabashin Indiya.

Hukumomin agaji na kasar a wannan Lahadi, sun ce mutane takwas ne suka mutu a yankin Assam, wasu tara a Arunachal Pradesh, mafi yawa daga cikinsu zabtarewar kasa ce ta rutsa da su.

Google search engine

Mahukunta sun fitar da gargadi ga wasu gundumomin da dama a gabascin Indiya, saboda mamakon ruwan sama a cikin kwanaki da suka gabata.

Ruwan saman ya sa kogin Brahmaputra ya cika ya tumbatsa, wanda ya taso daga yankin Himalayas har zuwa kasar Bangladesh.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara