DCL Hausa Radio
Kaitsaye

EFCC na binciken wasu mutane kan kudin jabu na Dala $899,800 a Kano

-

Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa a Nijeriya ta ce tana binciken wasu mutane biyu da ake zargi da tu’ammali da kudin jabu, inda ta ce an kama su da kudin Dala har $899,800.

Jami’an hukumar NDLEA ne dai suka kama Abubakar Hussaini da Sahabi Adamu a Wudil, kan titin zuwa Maiduguri jihar Borno kamar yadda EFCC ta wallafa a shafinta na X.

Google search engine

Sanarwar ta ce mutanen biyu na tafiya ne a cikin wata mota kirar Golf 3 kan hanyar zuwa kauyen Kila da ke karamar hukumar Gwaram a karamar hukumar Gwaram a jihar Jigawa.

Hukumar EFCC ta bayyana cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a kotu bayan kammala bincike.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara