DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyoyi 104 na son zama jam’iyyun siyasa a Nijeriya

-

Kungiyoyi 104 a Nijeriya ne suka mika bukatar a yi musu rajista don su zama jam’iyyun siyasa ga hukumar zaben INEC.

Kungiyoyin dai sun mika wannan bukata tasu ne bayan zaben shekarar 2023.

Google search engine

Binciken da jaridar Daily Trust ta yi, ya nuna cewa hukumar na ci gaba da jan kafa wajen yi wa jam’iyyun rejista.

Jaridar ta ruwaito cewa daya daga cikin hanyoyin da hadakar ‘yan adawa ke son bi wajen kalubalantar shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, shine fitowa da wata sabuwar jam’iyyar siyasa da za a yi wa rejista mai suna All Democratic Alliance (ADA).

A cewar majiyoyin daga cikin hadakar, wannan shine mafi dacewa saboda akwai zargin cewa jam’iyya mai mulki ta kutsa cikin galibin jam’iyyun adawa da ake da su, kuma za ta iya amfani da su wajen dakile yunkurin kawancen da ake shirin kullawa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara