DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutane 153 ne suka rasu a Ambaliyar Mokwa – NSEMA

-

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta ce adadin waɗanda suka mutu sakamakon ambaliya a Mokwa ya kai 153, bayan gano karin gawarwaki biyu a ƙarƙashin gada a ranar Asabar.

Shugaban hukumar, Dr Ibrahim Hussaini, ya ce gawarwakin an binne su ne da safiyar Lahadi. Ambaliyar dai ta afku ne ranar Laraba bayan ruwan sama mai ƙarfi da aka tafka a daren Talata, inda ta yi sanadin lalacewar dukiyoyi da rushewar wani ɓangare na gadar Mokwa da ke haɗa Arewa da Kudu maso Yamma.

Google search engine

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa tuni shugaban ƙasa Bola Tinubu ya tura tawagar gwamnati ƙarƙashin jagorancin Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, don jajanta wa gwamnatin Jihar Neja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara