DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ja kunnen ‘Sarkin Mota’ kan tsokanar ma’aikatan gwamnati a bidiyonsa

-

Gwamnatin tarayya ta gargadi dillalin motoci a Abuja, wanda aka fi sani da Alamin Sarkin Mota, kan yi wa ma’aikatan gwamnati ba’a a cikin bidiyon talla da yake yi.

Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa NOA ce ta yi wannan gargadi a cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban daraktanta, Lanre Issa-Onilu, a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Sarkin mota ya yi kaurin suna wajen bayyana cewa motocin da yake talla sun fi karfin ma’aikaci ya siya, saboda tsadarsu.

A saboda haka hukumar ta gargadi dillalin motocin da ya kiyaye irin kalaman da yake yi a duk lokacin da yake kokarin tallata motocinsa domin kaucewa cutar da jajirtattun ma’aikatan Nijeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara