Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da cewa kasar ba ta kai inda take mafarkin kaiwa ba tukuna, amma ya roki ’yan kasa da kada guiwarsu ta yi sanyi, akwai haske a gaba.
Shugaban kasar ya yi wannan rokon ne a cikin sakon Barka da Babbar Sallah da ya fitar.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa Babbar Sallah na tunatar da shugabanni irin nauyin da ke wuyansu.